Hankulan mutane a Kaduna ya tashi a yayin da yan bindiga suka kai hari filin tashin jiragen sama suka hana wani jirgi tashi daga filin.
Nigerian Tribune ta rawaito cewa, jirgin ya na shirin tashi ne zuwa Legas a ranar Asabar, a lokacin da bata garin suka kutsa titin jirgin hakan yasa ma’aikatan jirgin da fasinjoji suka tsere.
A cewar wata majiya da ta nemi a boye sunanta, yan bindigan sun harbi wani ma’aikacin hukumar kula da sararrin samaniyar Najeriya, NAMA.
Duk da cewa babu cikakken bayani game da harbin ma’aikacin, an gano cewa yan bindigan sun harbe shi ne a titin tashin jirgin.
A cewar rahoton jirgin da aka shirya ya tashi misalin karfe 12.30 na ranar Asabar ya fasa tashin saboda yan bindigan.