Rahotanni sun ce ƴan bindiga sun yi wa ofishin ƴan sanda a Nasko ƙofar rago tare da kashe DPO.
An kashe DPO Umar Mohammed Digari a ranar Talata da wasu ƴan sanda biyu, kamar yadda jaridar PRNigeria ta ruwaito.
Wata majiyar tsaro ta shaida wa jaridar cewa ƴan bindigar sun kai harin ramuwar gayya ne bayan harin da aka kai masu a maɓuyarsu inda aka ƙwace shanun da suka sato sama da 800.
Sai dai babu wata sanarwa daga rundunar ƴan sandan jihar da ta tabbatar da lamarin.