fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Wasu da ake zargi ‘yan IPOB ne sun jefa Bam a cikin kasuwar Imo

Date:

An samu rudani jiya a jihar Imo, bayan da rahotanni suka ce wasu ‘yan bindiga sun kai harin bam a babbar kasuwar Izombe da ke karamar hukumar Oguta a jihar.

An yi zargin cewa ’yan kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB) ne suka aiwatar da wannan danyen aikin da suka sanya dokar zama a gida a yankin.

Naija News ta rawaito cewa, a kalla motoci biyu ne ‘yan ta’addan suka kona sua. Lamarin da ya faru a cewar wani mazaunin garin da ya zanta da Daily Sun, ya sanya ‘yan kasuwa da kwastomomin da ke kasuwar suka rika tsira da rayukansu.

Majiyar ta shaida wa kafar yada labarai cewa, tun da farko ‘yan bindigar sun ziyarci kasuwar ne, domin gargadin ‘yan kasuwar kan illar fitowar su a ranar Litinin da ta gabata kan kasuwancinsu.

Bayan ‘yan mintuna kadan, an ce ‘yan bindigar sun sake tayar da zaune tsaye, inda suka kona motoci biyu da wuta a cikin kasuwar, lamarin da ya haifar da mummunar barna kafin a jefa bam a kasuwar.

Mutane da dama a cewar rahoton sun samu raunuka yayin da suke kokarin tserewa hatsarin.

“Sun zo ne suka jefa bam a cikin kasuwar, kowa ya fara gudu don tsira; sun zuba mai a kan motoci biyu kuma ko’ina ya tashi da wuta,” inji majiyar.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...

Lakurawa sun kashe Mutane 15 a Sokoto

Wasu da ake zargin mambobin ƙungiyar Lakurawa ne sun...

Dan wasan Liverpool Diago Jota da Kaninsa sun mu a hadarin mota

Ɗan wasan ƙwallon ƙafar Liverpool kuma ɗan ƙasar Portugal,...

Mun shirya tunkarar APC a 2027 – ADC

A ranar Laraba ne manyan ƴan adawar siyasa suka...

Mun dagulawa Iran lisafi na tsawon shekaru biyu a nukiliyar ta – Amurka

Ma'aikatar tsaron Amurka ta ce bayannan leken asirinta ya...

INEC za ta fitar da sabbin ƙa’idojin duba sakamakon zaɓe

A shirye-shiryen da take yi gabanin babban zaɓen Najeriya...
X whatsapp