fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Wasu da ake zargi ‘yan IPOB ne sun jefa Bam a cikin kasuwar Imo

Date:

An samu rudani jiya a jihar Imo, bayan da rahotanni suka ce wasu ‘yan bindiga sun kai harin bam a babbar kasuwar Izombe da ke karamar hukumar Oguta a jihar.

An yi zargin cewa ’yan kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB) ne suka aiwatar da wannan danyen aikin da suka sanya dokar zama a gida a yankin.

Naija News ta rawaito cewa, a kalla motoci biyu ne ‘yan ta’addan suka kona sua. Lamarin da ya faru a cewar wani mazaunin garin da ya zanta da Daily Sun, ya sanya ‘yan kasuwa da kwastomomin da ke kasuwar suka rika tsira da rayukansu.

Majiyar ta shaida wa kafar yada labarai cewa, tun da farko ‘yan bindigar sun ziyarci kasuwar ne, domin gargadin ‘yan kasuwar kan illar fitowar su a ranar Litinin da ta gabata kan kasuwancinsu.

Bayan ‘yan mintuna kadan, an ce ‘yan bindigar sun sake tayar da zaune tsaye, inda suka kona motoci biyu da wuta a cikin kasuwar, lamarin da ya haifar da mummunar barna kafin a jefa bam a kasuwar.

Mutane da dama a cewar rahoton sun samu raunuka yayin da suke kokarin tserewa hatsarin.

“Sun zo ne suka jefa bam a cikin kasuwar, kowa ya fara gudu don tsira; sun zuba mai a kan motoci biyu kuma ko’ina ya tashi da wuta,” inji majiyar.

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp