Wani abu ya fashewa a yankin Okene na jihar Kogi ya kashe mutane uku.
A cewar gidan talabijin na Channels, fashewar ta faru ne a safiyar ranar Alhamis a fadar Oyinoyi da ke karamar hukumar Okenne a jihar.
An samu labarin cewa jami’an ‘yan sanda na sashin yaki da bom sun isa wurin da lamarin ya faru.
A halin yanzu dai ana sa ran shugaban kasa Muhammadu Buhari zai ziyarci jihar a yau.
Zai kaddamar da wasu ayyuka a jihar ta Arewa ta tsakiya.