Salihu Tanko-Yakasai, tsohon mai taimakawa gwamna Abdullahi Ganduje na jihar Kano kan harkokin yada labarai, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar gwamnan jihar a zabe mai zuwa na 2023.
Tanko-Yakasai ya bayyana haka ta shafin sa na Twitter da aka tabbatar a ranar Talata.
Ya ce, sanarwar tasa a hukumance za ta gudana ne a ranar Juma’a, inda ya kara da cewa zai tsaya takara a jam’iyyar People’s Redemption Party (PRP).
“Da sunan Allah na dogara ga Allah; babu karfi sai ga Allah. Yan uwa da abokan arziki da masoyana, wannan shine in sanar daku aniya ta tsayawa takarar gwamnan jihar Kano karkashin babbar jam’iyyar mu ta PRP. Sanarwar ta a hukumance za ta faru a wannan Juma’a, ”ya wallafa a shafinsa na Twitter.
Hakan na zuwa ne makonni bayan da ya yi murabus daga mukaminsa na jam’iyyar APC.
A watan Fabrairun 2021, Ganduje ya kori Tanko-Yakasai saboda “ci gaba da maganganun da ba a kiyaye ba” da kuma sukar Shugaba Muhammadu Buhari.
Tanko-Yakasai, yayin da ya fice daga jam’iyyar APC a watan Maris, ya ce jam’iyyar ta kasa cika alkawuran da ta yi wa ‘yan Najeriya a yakin neman zabe.