Babban ɗakin taro na fadar shugaban ƙasa ya fara ɗaukar harama domin rantsar da sabbin ministocin gwamnatin shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu.
A watan Afrilu ne shugaban na Najeriya ya miƙa wa Majalisar Dattijan ƙasar sunayen mutum 45 domin tantantancewa a matsayin minsitoci.
Bayan haka nan shugaban na Najeriya ya bayyana ma’aikatun da kowane minista zai riƙe gabanin ranar ta yau da ake rantsarwar.
Sai dai ko a ranar Lahadi, shugaban ya fitar da wasu sauye-sauyen da ya yi na ma’aikatu ga wasu sabbin ministocin.
Wasu daga cikin ministocin da aka rantsar ya zuwa yanzu su ne:
Ministan wasanni – John Eno.
Ministan harkokin Neja-Delta, Abubakar Momoh.
Ministan ayyuka – David umahi
Ministan sufurin jiragen sama – Festus Keyamo
Ministar bayar da agaji da kawar da talauci – Betta Edu
Ministan ma’adanai, Dele Alake
Ministan kirkire-kirkire na kimiyya da fasaha – Uche Nnaji
Ministan harkokin cikin gida – Sa’idu A. Alkali
Ministan Masana’antu da ciniki da zuba jari – Doris Anite
Ministan tsaro – Muhammed Badaru Abubakar
Karamin Ministan Gidaje da Raya Birane – Abdullah T. Gwarzo
Ministar fasaha da al’adu – Hannatu Musawa
Ministan gidaje da raya birane – Ahmed M. Dangiwa
Karamar Ministar Babban Birnin Tarayya – Mairiga Mahmud
Ministan kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki – Atiku Bagudu