Gwamnan jihar Ekiti kuma shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya, Dr Kayode Fayemi zai bayyana takarar sa ta shugabancin kasa a ranar Laraba a Abuja.
Kamar yadda wata sanarwa da babban sakataren yada labaran sa, Yinka Oyebode ya sanyawa hannu, sanarwar ta ranar Laraba mai taken “Bayyana Ajandar Nijeriya”, ita ce kololuwar manyan shawarwarin da Gwamnan ya yi a shiyyar siyasa a cikin makonni shida da suka gabata.
“Dr Fayemi, bayan ya tattauna shirinsa na tsayawa takara a karo na daya da shugaban kasa Muhammadu Buhari a watan da ya gabata, ya nemi shawara, jagora da goyon baya daga shugabannin gargajiya da na siyasa a fadin jihohin kasar nan.” Sanarwar ta kara da cewa.