An sake zaben Cyril Ramaphosa a matsayin shugaban kasar Afirka ta Kudu a karkashin jam’iyyar African National Congress.
AriseTV ne ya ruwaito hakan a ranar Litinin.
Ramaphosa ya lashe zaben shugaban kasa da kuri’u 2,476 inda ya doke abokin takararsa, tsohon ministan lafiya, Zweli Mkhize.
Zaben nasa ya zo ne bayan da ‘yan hamayya suka nemi ya sauka daga mulki kan wata badakala da aka fi sani da ‘Farmscandal’ da ta hada da gano wasu makudan kudade a gonarsa.