Sanata Malam Ibrahim Shekarau ya karbi katin zama dan jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP).
Sanatan wanda ya sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa NNPP, ya fice daga jam’iyyar ne biyo bayan rikici tsakaninsa da tsagin jam’iyyar mai mulki ta jihar Kano.
Dubun dubatar magoya bayansa ne suka shelanta ficewar a a gidansa na Mundubawa.
Tsohon gwamnan jihar Kano kuma shugaban jam’iyyar NNPP, Rabi’u Musa Kwankwaso, wanda ya halarci taron sauya sheka a hukumance, ya mika masa katin zama dan jam’iyyar NNPP na Shekarau.
Wadanda suka halarci taron sun hada da masu ruwa da tsaki na siyasa da magoya bayansu da shugabannin majalisar Shura na gidan Malam Shekarau da sauran masu fada aji.