Shahararren malamin addinin musulunci kuma shugaban majalisar malamai ta Kano, Sheikh Ibrahim Khalil, ya koma jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).
Shugaban Jam’iyyar na Kano, Musa Shuaibu Ungoggo, ya tabbatar wa da NIGERIAN TRACKER ci gaban tare da Dokta Sai’du Ahmad Dukawa na Jami’ar Bayero Kano.
Shugaban Jam’iyyar ya ce, Sheikh Ibrahim Khalil ya shiga jam’iyyar ne tare da malamai takwas, domin ceto Kano daga rashin mulki da shan miyagun kwayoyi da magance barace-barace.
Musa Shuaibu Ungoggo ya kara da cewa, nan ba da dadewa ba Sakatariyar ADC ta kasa za ta shirya gagarumin liyafar tarbar, Sheikh Ibrahim Khalil da sauran su zuwa jam’iyyar.