Wani dan takarar gwamna a jam’iyyar APC a jihar Kaduna, Alhaji Sani Mohammed Sha’aban, ya yi watsi da sakamakon zaben fidda gwani da aka gudanar a ranar Alhamis, inda ya yi zargin cewa zaben na cike da kura-kurai.
A zaben fidda gwanin dan takarar gwamna a jihar Sanata Uba Sani ya samu kuri’u 1,149, yayin da Bashir Abubakar ya zo na biyu da kuri’u 37, Sha’aban ya zo na uku da kuri’u 10.
Da yake magana yayin wani taron manema labarai ranar Asabar a jihar Kaduna, Sha’aban ya yi watsi da tsarin. In ji talabijin din Channels.
Ya yi zargin cewa zaben ‘karade’ ne, domin akasarin wakilan kananan hukumomi 23 an kulle su ne a wajen da aka kada kuri’a tare da hana su zaben ‘yan takarar da suke so.