Sarki Salman bin Abdul Aziz na Saudiyya ya ayyana gobe Laraba a matsayin ranar hutu a faɗin ƙasar.
Ya bayar da hutun ne domin ‘yan ƙasar kama daga ma’aikatan gwamnati da masu zaman kansu da ɗalibai a dukkan matakan ilimi daban-daban na ƙasar, su samu damar yin murnar nasarar da ƙasar ta samu kan Argentina a gasar ƙwallaon ƙafa na diuniya da ke gudana a ƙasar Qatar.
A ranar Talata da rana ne ƙasar ta Saudiyya ta samu nasarar doke Argentina da ci 2-1 a wasan farko na cikin rukuni da suka fafata a filin wasa na Lusail.