An rantsar da Sanata Hassan Muhammad Nasiha, a matsayin mataimakin gwamnan Jihar Zamfara.
Alƙaliyar Alƙalai ta Zamfara Kulu Aliyu ce, ta rantsar da sanatan a yau Laraba bayan ‘yan majalisar dokokin jihar sun tsige Mahdi Aliyu Gusau daga muƙamin.
A yau Laraba ne dai bayan zaman majalisar dokokin jihar Zamfara ta tsige, mataimakin gwamna mai ci, sakamakon tuhume-tuhume da ake yi masa.
Sai dai a jawabin sa tsohon mataimakin gwamnan, Mahdi Aliyu Gusau, ya bayyana cewa, tsige shin na da nasaba ne ta kin komawa jam’iyyar APC, wanda ya gwammace ya zauna a jam’iyyar sa ta PDP.