Sabon mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Sanata Hussaini Nasiha, ya yi murabu daga mukamin sa na Sanata Mai wakiltar jihar Zamfara ta tsakiy.
Jaridar Punch ta rawaito cewa, Sanata Hussaini Nasiha, ya ɗauki wannan matakin ne, biyo bayan naɗa shi a matsayin sabon mataimakin gwamna da Gwamna Matawalle ya yi a Zamfara.
Nasiha ya maye gurbin, Barista Mahdi Aliyu Gusau, wanda a makon da ya gabata majaisar dokokin jihar ta tsige shi daga kan kujerarsa.
Da yake karantar wasikar da Sanatan ya aike wa majalisa a zamanta na yau, shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Lawan, ya sanar da murabus ɗin Nasiha.
Lawan ya sanar da cewa, Nasiha ya ajiye kujerarsa ta majalisar ne, domin ya zama mataimakin gwamnan Zamfara.