Jami’in Ukraine sun ce, dakarun Rasha sun yi nasarar kutsawa Kherson, wani gari da ke kudancin Ukraine.
Sai dai sun ce, har yanzu basu gama kwace shi ba tukunna.
Mai ba wa ma’aikatar harkokin cikin gida ta Ukraine shawara Vadym Denysenko, ya fadawa wani gidan talabijin din kasar cewa sojojin Ukraine na ci gaba da kokarin ganin garin bai kubce daga hannunsu ba.