fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Ranar Lahadi Litinin za a koma makarantu – Gwamnatin Kano

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta sanar da ranar Lahadi, 15 ga Satumba, 2024, a matsayin sabuwar ranar da za a koma makaratun kwana na firamare da na sakandare na gwamnati da kuma masu zaman kansu na zangon farko na shekarar 2024/2025.

Hakazalika ɗalibai a makarantun je-ka-ka-dawo a fadin jihar za su koma ranar Litinin 16 ga Satumba, 2024.

Idan dai ba a manta ba, kwamishinan ilimi na jihar Alhaji Umar Haruna Doguwa ne ya sanar a ranar Asabar 7 ga watan Satumba, ɗage ranar da za a koma makaranta.

A wata sanarwa da Daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi ta jihar, Balarabe Abdullahi Kiru ya fitar, gwamnatin jihar ta buƙaci iyaye da su yi la’akari da sabon ranar da za a koma makaranta domin tabbatar da cikakken bin doka da oda.

Sanarwar ta kuma shawarci ɗaliban da su guji shiga da abubuwan da ba a yarda da su ba a makarantunsu da kuma ya saɓawa doka, kamar irin su wuƙaƙe ko reza, kuma su tabbatar da bin doka.

Sanarwar ta jaddada ƙudirin gwamnatin jihar na ganin kowane yaro ya samu ilimi mai inganci.

the nation newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp