Jam’iyyar PDP ta mika sunayen mutane biyu da ta tantance, domin maye gurbin gwamnan jihar Ebonyi, David Umahi da mataimakinsa ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).
A safiyar ranar Talata ne mai shari’a Inyang Ekwo na babbar kotun tarayya da ke Abuja ya bayar da umarnin tsige Umahi daga mukaminsa sakamakon sauya sheka da ya yi zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a watan Nuwamba 2020.
Ya ci gaba da cewa, kundin tsarin mulkin kasar bai amince da mika katin zabe daga wata jam’iyya zuwa wata ba.
Alkalin ya kuma umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta karbi sunayen mutane biyu daga jam’iyyar PDP da za su maye gurbin Umahi da Eric Igwe a matsayin gwamna da mataimakin gwamna.
Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a wani taron manema labarai a Abuja, ya ce jam’iyyar ta zabi Iduma Igariwe da Fred Udogwu a matsayin gwamnan Ebonyi kuma mataimakin gwamna ga INEC.
Ayu ya ce: “Bayan shawarwarin da shugabannin jam’iyyar na kasa suka yi da sauran masu ruwa da tsaki, mun yanke shawarar gabatar da Hon. Iduma Igariwe da Fred Udogwu na mukaman gwamna da mataimakin gwamna a jihar Ebonyi.”