fidelitybank

Da Dumi-Dumi: PDP ta mika sunayen mutane 2 da za su maye gurbin gwamnan Ebonyi

Date:

Jam’iyyar PDP ta mika sunayen mutane biyu da ta tantance, domin maye gurbin gwamnan jihar Ebonyi, David Umahi da mataimakinsa ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

A safiyar ranar Talata ne mai shari’a Inyang Ekwo na babbar kotun tarayya da ke Abuja ya bayar da umarnin tsige Umahi daga mukaminsa sakamakon sauya sheka da ya yi zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a watan Nuwamba 2020.

Ya ci gaba da cewa, kundin tsarin mulkin kasar bai amince da mika katin zabe daga wata jam’iyya zuwa wata ba.

Alkalin ya kuma umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta karbi sunayen mutane biyu daga jam’iyyar PDP da za su maye gurbin Umahi da Eric Igwe a matsayin gwamna da mataimakin gwamna.

Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a wani taron manema labarai a Abuja, ya ce jam’iyyar ta zabi Iduma Igariwe da Fred Udogwu a matsayin gwamnan Ebonyi kuma mataimakin gwamna ga INEC.

Ayu ya ce: “Bayan shawarwarin da shugabannin jam’iyyar na kasa suka yi da sauran masu ruwa da tsaki, mun yanke shawarar gabatar da Hon. Iduma Igariwe da Fred Udogwu na mukaman gwamna da mataimakin gwamna a jihar Ebonyi.”

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp