fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Olise Metuh ya ficce daga PDP

Date:

Olisa Metuh, tsohon sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa ya fice daga jam’iyyar.

Metuh ya bayyana cewa zai kara ba da gudunmawa ga harkokin mulkin Najeriya ta hanyar rashin bangaranci.

A wata wasika da ya aikewa shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu, Metuh ya koka da yadda siyasar Najeriya ke tabarbarewa.

Ya yi nuni da cewa ba zai iya kara shiga harkokin siyasar bangaranci ba.

A cewar Metuh: “A ziyarar da na yi na tsawon makonni uku saboda dalilai na lafiya da na kashin kai, na fahimci cewa ba zan iya kara yin siyasa ba a Najeriya.

“Dalilin da ya sa na yanke wannan shawara shi ne, daga gogewa na da kuma yanayin siyasa da ci gaban Najeriya, na yi imanin cewa zan kara ba da gudummawa ga dimokuradiyya da shugabanci na gari a Najeriya ta hanyar rashin bangaranci.

“A kan haka, na rubuta cikin girmamawa domin in sanar da ku ficewara daga jam’iyyar PDP da kuma daina siyasar bangaranci.

“Kamar yadda kundin tsarin mulkin PDP ya tanada, na mika kwafin murabus na ga shugaban gunduma ta.”

A shekarar 2016, Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati, EFCC, ta gurfanar da shi a gaban kuliya bisa zargin almundahanar Naira miliyan 400.

EFCC dai ta zargi Metuh da karbar makudan kudade daga ofishin tsohon mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, NSA.

Sai dai Metuh ya musanta karbar kudaden, yana mai jaddada cewa tsohon ofishinsa ne ya tattara kudaden ya kuma yi amfani da su wajen gurfanar da shi gaban kotu.

Duk da musanta zargin, an yanke wa tsohon kakakin PDP hukuncin zaman gidan yari a shekarar 2021 bayan an same shi da laifuka bakwai na karkatar da kudade.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Kano ta gargadi Matasa da ‘yan Gwangwan kan sayen kayan gwamnati

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi matasa da ’yan kasuwa...

NIMET ta gargai Borno kan ambaliya da sauran jihohi

A baya-bayan nan ne hukumar hasashen yanayi ta Najeriya...

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...
X whatsapp