Mutane da dama sun makale a halin yanzu yayin da wani bene mai hawa uku ya ruguje a Legas yayin da aka yi ruwan sama kamar da bakin kwarya.
Ginin wanda ke Lamba 4 Alayaki Lane, Legas Island, ya rufta a ranar Asabar.
Hukumamomi sun ce an ceto mutane biyu da ransu yayin da aka kwashe gawar mutum daya, yayin da mutane da dama suka makale.
Babban Sakatare na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas, LASEMA, Dokta Femi Oke-Osanyintolu, ya shaida wa PM NEWS cewa, hukumar ta mayar da martani kan lamarin wanda tuni ya saba wa ka’idojin tsaro.