fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Mutane hudu sun mutu 12 sun jikkata a fashewar Tankar Mai

Date:

Ana fargabar mutane hudu sun mutu, yayin da wasu 12 suka samu raunuka daban-daban, sakamakon fashewar wani abu a kasuwar sinadarai ta Onitsha a ranar Talata.

Majiyoyi sun shaidawa DAILY POST cewa, fashewar ta yi sanadin tashin gobara a yankin, tare da lalata kayayyaki sama da Naira miliyan 850 a cikin aikin.

Fashewar ta afku ne da misalin karfe 12:45 na rana a kasuwar, lamarin da ya kai ga turmutsutsu, daga bisani kuma ta yi aman wuta, kamar yadda wata majiya ta bayyana.

Ya kara da cewa mutane hudun sun mutu ne sakamakon turmutsitsin da ‘yan kasuwa suka yi domin tsira da rayukansu.

“Shugaban karamar hukumar Onitsha ta Kudu, Mista Emeka Orji ya tuntubi shugaban hukumar kashe gobara na jihar Anambra, Martin Agbili, wanda ya tura jami’an sashen daga Okpoko a karamar hukumar Ogbaru da kuma na Asaba a jihar Delta.

“Shugaban majalisar ya kuma tuntubi Baturen ‘yan sanda Fegge, Rabi’u Garuba wanda ya tura jami’ai da mazaje kasuwar domin tabbatar da tsaron kayayyaki da sauran kadarorin ‘yan kasuwar,” inji majiyar.

Wani dan kasuwa wanda ya zanta da wannan dan jarida, Mista Nweke Uchenna ya ce: “Muna cikin shagunanmu kamar yadda muka saba sai muka ji wata kara kamar tashin bam sai muka ga hayaki mai kauri daga wasu shaguna a sama, kowa ya fara gudu don tsira.

“Daga nan sai mutane suka fara ihun neman agaji, sai muka ga mutane dauke da ‘yan kasuwa daga cikin shagunan da suka kone, wasu kuma sun kone kurmus, yayin da wasu da alamun hayaki da turmutsutsun suka shake su.

“Ba mu san nawa ne gobarar ta yi hasarar ba amma ana iya kiyasin Naira miliyan 850 zuwa kusan Naira biliyan 1 saboda kayayyakin suna da karfi da sinadarai da ke da zafi sosai,” inji shi.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Anambra, DSP Toochukwu Ikenga ne ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce: “Ba a tabbatar da adadin wadanda suka mutu ba a yanzu, amma jami’an mu karkashin jagorancin DCP John Ogbodoaga suna nan, kuma an shawo kan lamarin.”

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp