Mutum biyu cikin wadanda ake tuhuma da mu’amalla da hodar Ibilis a shari’ar da aka gurfanar da Abba Kyari tare da wasu mutu shida sun amsa laifukan da ake tuhumarsu da aikatawa.
Mutane biyun ba sa cikin ‘yan sanda hudun da ake tuhuma tare da babban jami’in ‘yan sandan.
Kamar yadda jaridar Premium Times ta rawaito cewa, mutanen biyu wato Chibuna Umeibe da Emeka Ezenwanne sun ba lauyoyinsu mamaki bayan da suka amsa laifukan da ake tuhumarsu da aikatawa.