Hukumomin Saudiyya sun ware wa Najeriya kason maniyyata 43,008, domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2022.
Shugaban Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON), Alhaji Zhikrullah Kunle Hassan, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis yayin da yake ganawa da shugaban hukumar jin dadin alhazai da hukumomi da kuma kwamitoci a Abuja.
A cewarsa, “Akan rabon, jihohin suna da 33, 976 yayin da masu yawon bude ido ke da 9,032.”
Ya kuma jaddada cewa dole ne a yi rajistar dukkan maniyyatan ta hanyar Intanet ta hanyar E-Hajj da tsarin aikin Hajji da sauran manhajoji.
NAHCON ta kuma yi nuni da cewa nan ba da dadewa ba za a samar da duk ka’idojin yin rajista sannan kuma duk wata hanya ta rajista za ta kasance a bisa ka’ida.