Rahotanni daga kasar Ukriane na nuni da cewa, wani harin makamin roka da Rasha ta kai ya kashe mutane 11 a Kharkiv, in ji jami’an yankin.
Shugaban hukumar kula da yankin na Kharkiv, Oleg Synegubov, ya ce, akalla mutane 11 ne suka mutu, yayin da wasu da dama suka jikkata, yayin da wasu makaman roka da Rasha ta harba a gabashin kasar ta Ukraine suka sauka a wasu unguwannin jama’a.
Kharkiv, wanda shine birni na biyu mafi girma a kasar Ukraine, ya zama É—aya daga cikin manyan fagagen daga da Moscow ta kaddamar da mamaya.