Ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Dr. Chris Ngige ya janye daga takarar neman kujerar shugaban kasa Muhammadu Buhari a 2023.
Ya bayyana janyewa daga takarar ne domin samun tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a a Abuja.
Sanarwar ta Ngige ta biyo bayan wani taro ne da aka gudanar a dakin taro na fadar shugaban kasa da ke babban birnin kasar, domin karrama ministocin da ke neman mukaman zabe a zaben 2023 mai zuwa. A cewar talabijin na Channels.