Mayakan kungiyar ISWAP da iyalansu 104 sun mika wuya ga dakarun sojojin Najeriya.
‘Yan ta’addar da suka mika kansu a ranar Asabar, 5 ga watan Fabrairu, sun hada da maza 22, mata 27 da kuma yara 55.
Shelkwatar rundunar soji ce, ta tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar a shafinta na Facebook a ranar Litinin, 7 ga watan Fabrairu, ta bayyana cewa, mayakan da suka mika wuya sun hada da maza 22 da mata 27 da yara 55.
Rundunar sojin ta kuma bayyana cewa, yan ta’addan da kansu ne suka mika wuya ga dakarun runduna ta musamman ta 25 a yankin Damboa da ke Jihar Borno.