fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Matashi ya nutse a cikin ruwan Legas

Date:

Wani matashi dan shekara 26 mai suna Olamilekan Olubusade, ya nutse a ruwa a wani wurin shakatawa a tekun Alpha da ke jihar Legas a Najeriya.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Benjamin Hundeyin, ne ya tabbatar da afkuwar lamarin in da ya ce har yanzu ba a gano gawarsa ba.

Olamilekan Olubusade,ya nutse ne a yayin da yake ninkaya tare da abokansa.

Jami’in dan sandan ya ce, sun samu labarin nutsewar matashin ne a ranar Talata, bayan ‘yan uwansa sun kai rahoto ofishin ‘yan sanda.

Ya ce daga bayanan da suka samu daga wajen ‘yan uwan mamacin, matashin ya je tekun ne a ranar Litinin din da ta wuce tare da abokansa.

Wannan lamari dai ya zo ne kwanaki bayan da wasu matasa hudu suka nutse a ruwa a lokacin da suke murnar kammala jarrabawar sakandare a jihar.

A yanzu haka dai gwanayen ninkaya na ci gaba da bincike da nufin gano gawar matashin.

A gefe guda kuma ana ci gaba da gudanar da bincike akai.

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...
X whatsapp