Wani matashi dan shekara 26 mai suna Olamilekan Olubusade, ya nutse a ruwa a wani wurin shakatawa a tekun Alpha da ke jihar Legas a Najeriya.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Benjamin Hundeyin, ne ya tabbatar da afkuwar lamarin in da ya ce har yanzu ba a gano gawarsa ba.
Olamilekan Olubusade,ya nutse ne a yayin da yake ninkaya tare da abokansa.
Jami’in dan sandan ya ce, sun samu labarin nutsewar matashin ne a ranar Talata, bayan ‘yan uwansa sun kai rahoto ofishin ‘yan sanda.
Ya ce daga bayanan da suka samu daga wajen ‘yan uwan mamacin, matashin ya je tekun ne a ranar Litinin din da ta wuce tare da abokansa.
Wannan lamari dai ya zo ne kwanaki bayan da wasu matasa hudu suka nutse a ruwa a lokacin da suke murnar kammala jarrabawar sakandare a jihar.
A yanzu haka dai gwanayen ninkaya na ci gaba da bincike da nufin gano gawar matashin.
A gefe guda kuma ana ci gaba da gudanar da bincike akai.