fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Matar gwamna mai barin gado ta mari wata mata yayin da aka karbi mulki a wajen mijin ta

Date:

Abun alajabi ya faru a wurin bikin rantsar da Farfesa Chukwuma Soludo a matsayin gwamnan Anambra lokacin da uwargidan gwamna Willie Obiano mai barin gado, Ebelechukwu ta mari Misis Bianca Ojukwu a wajen taron.

Wakilin NAN da ke wurin taron ya ruwaito cewa, lamarin ya faru ne bayan da Soludo ya rantsar da shi.

Tuni dai manyan baki da suka hada da Obiano suka zauna a lokacin da Mrs Obiano ta shiga wajen, sannan ta zarce a layin gaba inda matar Dim Odumegwu Ojukwu ta zauna kusa da ita ta kuma mare ta.

Matakin ya ja hankalin jami’an tsaro da wasu mutane da suka janye Misis Obiano daga hannun Bianca wadda ta yi matukar kaduwa da matakin.

Daga baya an tafi da Mrs Obiano, kuma jim kadan, mijin nata ya bar wurin tun da lamarin ya faru bayan an rantsar da sabon gwamnan.

DAILY POST ta ruwaito cewa babban alkalin jihar, Mai shari’a Onochie Anyachebelu ne ya rantsar da Soludo da misalin karfe 9:45 na safe a fadar gwamnatin jihar Anambra.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin Æ´an Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama Æ´an Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na Æ™asa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...
X whatsapp