Matar jami’in dan sandan da aka dakatar, DCP Abba Kyari, ta yanke jiki ta fadi a cikin harabar babbar kotun tarayya dake birnin Abuja.
Matar, sanya da bakin Hijabi ta yanke jiki ta fadi ne lokacin da Alkali Emeka Nwite ya yi watsi da bukatar belin Abba Kyari, bisa zargin safarar hodar iblis da ake masa.
Matar ta yanke jiki ne lokacin da jami’an NDLEA suka tasa keyar Abba Kyari da sauran wadanda a ke zargi daga cikin kotun, in ji rahoton Vanguard.
Wasu jami’an NDLEA da lauyoyi su ka yi gaggawan daukarta daga wajen, kuma suka shigar da ita daya daga cikin ofishohin dake cikin kotu.
Sai dai an yi kokarin samar mata abin shaka, lokacin da matan da suka rako ta kotu suka ce ta na fama da cutar nimfashi ta asma.