Mataimakin shugaban Najeriya Yemi Osinbajo ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2023.
Ya bayyana hakan ne a wani takaitaccen yada labarai da aka yada ta shafinsa na Twitter bayan shafe tsawon watanni ana ta cece-kuce.
Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa Osinbajo, a liyafar cin abincin dare da ya shirya a fadar shugaban kasa a Villa, domin buda azumin watan Ramadan a ranar Lahadi, ya sanar da gwamnonin APC shirinsa na ya gaji maigidansa, Manjo Janar Muhammadu Buhari (mai ritaya), wanda wa’adin shugabancinsa zai kare nan da watanni 13.
Ya ce, “Na yi imanin cewa, dalilin da ya sa Allah Madaukakin Sarki Ya ba ni wadannan abubuwan da suka faru, da wadannan bayanai da kuma wadannan damammaki shi ne, dole ne a yi amfani da su wajen amfani da wannan kasa tamu mai girma da kuma al’ummarta masu girma.
“A dalilin haka ne a yau, cikin tawali’u, a hukumance na bayyana aniyara ta tsayawa takarar shugaban kasa a tarayyar Najeriya a karkashin babbar jam’iyyarmu ta All Progressives Congress.”
Osinbajo, wanda ya cika shekaru 65 a watan da ya gabata, babban mai ba da shawara ne ga Najeriya, kuma tsohon malami ne a jami’ar Legas. Shi ma babban Fasto ne a Cocin Redeemed Christian Church of God.
Ya fara aikin gwamnati ne a shekarar 1988 a matsayin mai ba da shawara (shawarwari da shari’a) ga babban mai shari’a kuma ministan shari’a, Bola Ajibola, mukamin da ya rike tsawon shekaru hudu.