fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Mataimakin shugaban kasa ya ce zai gaji kujerar Buhari a 2023

Date:

Mataimakin shugaban Najeriya Yemi Osinbajo ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2023.

Ya bayyana hakan ne a wani takaitaccen yada labarai da aka yada ta shafinsa na Twitter bayan shafe tsawon watanni ana ta cece-kuce.
Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa Osinbajo, a liyafar cin abincin dare da ya shirya a fadar shugaban kasa a Villa, domin buda azumin watan Ramadan a ranar Lahadi, ya sanar da gwamnonin APC shirinsa na ya gaji maigidansa, Manjo Janar Muhammadu Buhari (mai ritaya), wanda wa’adin shugabancinsa zai kare nan da watanni 13.

Ya ce, “Na yi imanin cewa, dalilin da ya sa Allah Madaukakin Sarki Ya ba ni wadannan abubuwan da suka faru, da wadannan bayanai da kuma wadannan damammaki shi ne, dole ne a yi amfani da su wajen amfani da wannan kasa tamu mai girma da kuma al’ummarta masu girma.

“A dalilin haka ne a yau, cikin tawali’u, a hukumance na bayyana aniyara ta tsayawa takarar shugaban kasa a tarayyar Najeriya a karkashin babbar jam’iyyarmu ta All Progressives Congress.”

Osinbajo, wanda ya cika shekaru 65 a watan da ya gabata, babban mai ba da shawara ne ga Najeriya, kuma tsohon malami ne a jami’ar Legas. Shi ma babban Fasto ne a Cocin Redeemed Christian Church of God.

Ya fara aikin gwamnati ne a shekarar 1988 a matsayin mai ba da shawara (shawarwari da shari’a) ga babban mai shari’a kuma ministan shari’a, Bola Ajibola, mukamin da ya rike tsawon shekaru hudu.

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp