Mataimakin gwamnan jihar Katsina, Mannir Yakubu ya yi murabus daga mukaminsa na kwamishinan noma da albarkatun kasa.
Wata sanarwa da babban sakataren yada labaran sa, Ibrahim Kallah ya fitar a jiya, ta ce, Yakubu ya yi murabus ne bisa ga sashe na 84 (12) na dokar zabe ta 2022 da aka yi wa gyara.
Ya ce: “Mannir ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis, 14 ga Afrilu, 2022, a shirye-shiryen sa na ayyana takarar gwamna nan ba da dadewa ba.”
Sanarwar ta kara da cewa, mataimakin gwamnan ya godewa Allah Madaukakin Sarki da Gwamna Aminu Masari da suka ba shi damar bayar da gudunmuwar “domin dawo da aikin gona a gwamnatin Masari.