Masu garkuwa da mutanen sun sako malamin jami’ar da aka sace a jami’ar kimiyya da fasaha ta Kano (KUST) Wudil, Huzaifa Karfi.
An saki Karfi ne da yammacin ranar Asabar. An yi garkuwa da shi ne a Zariya ranar Laraba a lokacin da ya je kai kudin fansa ga hakimin Karfi da ke karamar hukumar Takai a Kano, Abdulyahyah Ilu, wanda daga nan ya samu ‘yanci.
A baya dai an ruwaito cewa wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki tare da kashe mutane shida a kauyen Karfi da ke karamar hukumar Takai a jihar Kano tare da yin garkuwa da basaraken mai shekaru 53 a duniya.
An ce ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyen ne a kan babura uku daga jihar Bauchi ta dajin Ringim da ke Jigawa.
Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, wakilinmu ya samu labarin cewa malamin da aka saki tare da wasu na kan hanyarsu ta komawa Kano.