A kalla mutane 23 da suka hada da mata biyu da ’ya’yan tsohon akawun jihar Zamfara, Alhaji Abubakar Bello, wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da su a garin Furfuri da ke karamar hukumar Bungudu a jihar.
Wani mazaunin yankin mai suna Malam Haruna Manaja Furfuri a wata hira da Blueprint ya ce ‘yan bindigar sun yiwa garin kawanya ne da misalin karfe 2:30 na safiyar ranar Litinin.
A cewarsa, ‘yan bindigar sun je gidan tsohon akanta janar na Zamfara, inda suka yi garkuwa da matansa biyu, ‘ya’ya uku a yayin harin.
Malam Manaja ya kara da cewa matan biyu da aka yi garkuwa da su da sauran matan sun tsere bayan ‘yan sa’o’i da sace su.
“Bayan da jama’a suka bi sawun barayin cikin daji ne ‘yan fashin suka bar wadanda abin ya shafa suka gudu. Haka aka kubutar da wasu daga cikin wadanda aka sace da suka hada da mata biyu na Alhaji Abubakar Bello,” inji shi.
Ya ce har yanzu ‘ya’yan tsohon akantan janar din su uku har da wata budurwa da za a yi aure ba da jimawa ba suna cikin gidan ‘yan fashi.
“Kamar yadda nake magana da ku yanzu, ‘yan fashin sun amsa ta wayar tarho suna neman kudi daga hannun akawun janar din a matsayin kudin fansa kafin su saki ‘ya’yansa uku,” inji shi.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, SP. Muhammad Shehu, a wata hira da Blueprint ya tabbatar da faruwar lamarin.