fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Masu garkuwa sun kama mutane 23 ciki harda ‘ya’yan tsohon akanta na Zamfara

Date:

A kalla mutane 23 da suka hada da mata biyu da ’ya’yan tsohon akawun jihar Zamfara, Alhaji Abubakar Bello, wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da su a garin Furfuri da ke karamar hukumar Bungudu a jihar.

Wani mazaunin yankin mai suna Malam Haruna Manaja Furfuri a wata hira da Blueprint ya ce ‘yan bindigar sun yiwa garin kawanya ne da misalin karfe 2:30 na safiyar ranar Litinin.

A cewarsa, ‘yan bindigar sun je gidan tsohon akanta janar na Zamfara, inda suka yi garkuwa da matansa biyu, ‘ya’ya uku a yayin harin.

Malam Manaja ya kara da cewa matan biyu da aka yi garkuwa da su da sauran matan sun tsere bayan ‘yan sa’o’i da sace su.

“Bayan da jama’a suka bi sawun barayin cikin daji ne ‘yan fashin suka bar wadanda abin ya shafa suka gudu. Haka aka kubutar da wasu daga cikin wadanda aka sace da suka hada da mata biyu na Alhaji Abubakar Bello,” inji shi.

Ya ce har yanzu ‘ya’yan tsohon akantan janar din su uku har da wata budurwa da za a yi aure ba da jimawa ba suna cikin gidan ‘yan fashi.

“Kamar yadda nake magana da ku yanzu, ‘yan fashin sun amsa ta wayar tarho suna neman kudi daga hannun akawun janar din a matsayin kudin fansa kafin su saki ‘ya’yansa uku,” inji shi.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, SP. Muhammad Shehu, a wata hira da Blueprint ya tabbatar da faruwar lamarin.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp