fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Masu garkuwa da mutane sun sace mutane 18 a hanyar Abuja

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, sun tare wata motar bas mai mutane 18, a kauyen Ochonyi- Omoko, daura da babbar hanyar Abuja zuwa Lokoja a jihar Kogi.

Wani fasinja Benjamin Isaac da ya tsere ya ce, lamarin ya faru ne da misalin karfe 8:03 na daren Laraba.

Ya ce, maharan da suka boye a cikin daji sun bude wuta kan motar bas din, inda suka lalata tayoyin baya a cikin aikin.

“Sun bude wuta a kan tayoyin baya, lamarin da ya tilasta wa direban ya rasa yadda zai yi. A lokacin da direban motar ya kauce hanya, ‘yan bindigar sun fito daga inda suka buya suka umarci fasinjojin da su fito. Sun kai mu cikin daji da bindiga,” in ji shi, ya kuma kara da cewa ya yi nasarar tserewa tare da wasu fasinjojin da suka gudu cikin daji.

Isaac ya ce, ya hau motar bas ne a gefen titi a Zuba, a lokacin da yake tafiya zuwa Okpella, jihar Edo.

Wani dan banga da ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce yana alwala gabanin Sallar Isha’i ne, sai ya ji karar harbe-harbe.

“Bayan addu’a na ne na tuntubi abokan aikina kuma na zagaya wurin da lamarin ya faru, inda muka gano wata motar bas da ta yashe a gefen hanya ba tare da fasinjoji a ciki ba,” ya ce daga baya ya gano cewa an sace wasu fasinjojin da ke cikin motar.

Majiyar ‘yan banga ta ce, shi da abokan aikinsa na ci gaba da tseratar dajin domin zakulo ‘yan bindigar da kuma ceto wadanda lamarin ya rutsa da su.

Rundunar ‘yan sandan jihar dai ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba. Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Kogi, DSP Williams Ovye Ayah, har yanzu bai amsa kiran da aka yi masa da sakon da aka tura mas ba, kamar yadda The Will. ta rawaito.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp