fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Manchester United ta sallami Ronaldo

Date:

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ta sallami dan wasan Portugal, Cristiano Ronaldo, nan take.

Matakin dai ya biyo bayan wata tattaunawa mai cike da cece-kuce da dan wasan mai shekaru 37 ya soki kungiyar kuma ya ce, ba ya mutunta kocin kungiyar Erik ten Hag.

Bangarorin biyu sun bayyana cewa sallamar ta Ronaldo “an amince da juna nan take”.

Sanarwar da Manchester United ta fitar ta ce “Kungiyar ta gode masa saboda gagarumar gudunmawar da ya bayar tsawon shekaru biyu a Old Trafford.”

Sun yi fatan alheri ga “shi da iyalinsa a nan gaba” kuma sun kara da cewa “kowa a Manchester United ya ci gaba da mai da hankali kan ci gaba da kai kungiyar a karkashin Erik ten Hag da kuma yin aiki tare, domin samar da nasara a filin wasa”.

“Bayan tattaunawa da Manchester United mun amince tare da kawo karshen kwantiragin mu da wuri,” in ji wata sanarwa daga dan wasan.

“Ina son Manchester United kuma ina son magoya baya, hakan ba zai taba canzawa ba. Duk da haka, ya  na jin lokacin da ya dace da ni domin neman sabon kalubale.

“Ina yiwa kungiyar fatan samun nasara a sauran kakar wasanni da kuma nan gaba.”

Ronaldo ya na tare da Portugal a gasar cin kofin duniya da ake yi a Qatar kuma ya na shirin jagorantar su a wasan farko na rukunin H da Ghana ranar Alhamis.

dailysun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baɗala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...
X whatsapp