fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Manchester United ta sallami Ronaldo

Date:

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ta sallami dan wasan Portugal, Cristiano Ronaldo, nan take.

Matakin dai ya biyo bayan wata tattaunawa mai cike da cece-kuce da dan wasan mai shekaru 37 ya soki kungiyar kuma ya ce, ba ya mutunta kocin kungiyar Erik ten Hag.

Bangarorin biyu sun bayyana cewa sallamar ta Ronaldo “an amince da juna nan take”.

Sanarwar da Manchester United ta fitar ta ce “Kungiyar ta gode masa saboda gagarumar gudunmawar da ya bayar tsawon shekaru biyu a Old Trafford.”

Sun yi fatan alheri ga “shi da iyalinsa a nan gaba” kuma sun kara da cewa “kowa a Manchester United ya ci gaba da mai da hankali kan ci gaba da kai kungiyar a karkashin Erik ten Hag da kuma yin aiki tare, domin samar da nasara a filin wasa”.

“Bayan tattaunawa da Manchester United mun amince tare da kawo karshen kwantiragin mu da wuri,” in ji wata sanarwa daga dan wasan.

“Ina son Manchester United kuma ina son magoya baya, hakan ba zai taba canzawa ba. Duk da haka, ya  na jin lokacin da ya dace da ni domin neman sabon kalubale.

“Ina yiwa kungiyar fatan samun nasara a sauran kakar wasanni da kuma nan gaba.”

Ronaldo ya na tare da Portugal a gasar cin kofin duniya da ake yi a Qatar kuma ya na shirin jagorantar su a wasan farko na rukunin H da Ghana ranar Alhamis.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp