Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ta sallami dan wasan Portugal, Cristiano Ronaldo, nan take.
Matakin dai ya biyo bayan wata tattaunawa mai cike da cece-kuce da dan wasan mai shekaru 37 ya soki kungiyar kuma ya ce, ba ya mutunta kocin kungiyar Erik ten Hag.
Bangarorin biyu sun bayyana cewa sallamar ta Ronaldo “an amince da juna nan take”.
Sun yi fatan alheri ga “shi da iyalinsa a nan gaba” kuma sun kara da cewa “kowa a Manchester United ya ci gaba da mai da hankali kan ci gaba da kai kungiyar a karkashin Erik ten Hag da kuma yin aiki tare, domin samar da nasara a filin wasa”.
“Bayan tattaunawa da Manchester United mun amince tare da kawo karshen kwantiragin mu da wuri,” in ji wata sanarwa daga dan wasan.
“Ina son Manchester United kuma ina son magoya baya, hakan ba zai taba canzawa ba. Duk da haka, ya na jin lokacin da ya dace da ni domin neman sabon kalubale.
“Ina yiwa kungiyar fatan samun nasara a sauran kakar wasanni da kuma nan gaba.”
Ronaldo ya na tare da Portugal a gasar cin kofin duniya da ake yi a Qatar kuma ya na shirin jagorantar su a wasan farko na rukunin H da Ghana ranar Alhamis.