fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Malaman Sakandire da Firamare za su tsunduma yajin aiki

Date:

Malaman Firamare da na Sakandare a fadin kasar Ghana sun ce, za su tsunduma yajin aiki saboda rashin biyan su kudaden su na alawus.

Malaman dai sun ce kudaden na alawus, wanda kashi 20 na albashinsu, yana da muhimmanci sosai domin zai rage musu wahala daga halin tabarbarewar tattalin arziki da kasar ke ciki.

Karuwar hauhawarar farashi da kasar ke fama da shi dai ba a taba ganin irin sa ba a cikin shekara 18, inda kasar mai albarkatun kasa da ke Afrika ta Yamma ke shirin ciyo bashi domin samun damar biyan ma’aikatan ta.

Ana sa ran wata tawaga daga asusun bada lamuni na duniya, IMF, za ta kai ziyara Ghana a makon nan domin fara tattaunawa da gwamnatin kasar domin taimaka mata.

Yajin aikin da malaman da ke koyarwa suka ayyana a yau Litinin ya shafi har da wadanda ba sa koyarwa.

Wannan na zuwa ne bayan da gwamnatin Ghana ta gaza aiwatar da yarjejeniyar da ta cimma da shugabannin malaman suka ba ta ranar 30 ga watan Yuni. In ji BBC.

legit news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp