fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Malaman Sakandire da Firamare za su tsunduma yajin aiki

Date:

Malaman Firamare da na Sakandare a fadin kasar Ghana sun ce, za su tsunduma yajin aiki saboda rashin biyan su kudaden su na alawus.

Malaman dai sun ce kudaden na alawus, wanda kashi 20 na albashinsu, yana da muhimmanci sosai domin zai rage musu wahala daga halin tabarbarewar tattalin arziki da kasar ke ciki.

Karuwar hauhawarar farashi da kasar ke fama da shi dai ba a taba ganin irin sa ba a cikin shekara 18, inda kasar mai albarkatun kasa da ke Afrika ta Yamma ke shirin ciyo bashi domin samun damar biyan ma’aikatan ta.

Ana sa ran wata tawaga daga asusun bada lamuni na duniya, IMF, za ta kai ziyara Ghana a makon nan domin fara tattaunawa da gwamnatin kasar domin taimaka mata.

Yajin aikin da malaman da ke koyarwa suka ayyana a yau Litinin ya shafi har da wadanda ba sa koyarwa.

Wannan na zuwa ne bayan da gwamnatin Ghana ta gaza aiwatar da yarjejeniyar da ta cimma da shugabannin malaman suka ba ta ranar 30 ga watan Yuni. In ji BBC.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke É—auka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da Æ™arfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar Æ´ansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naÉ—a kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka Æ´anbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe Æ´anbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...
X whatsapp