Biyo bayan karewar yajin aikin da ta yi na makonni biyu, kungiyar malaman makarantun kwalejin kimiya ta kasa (ASUP) ta umurci mambobinta da su koma bakin aiki a ranar Litinin 30 ga watan Mayu, 2022.
Kungiyar ta ce ta dauki matakin ne biyo bayan wasu ci gaba da aka samu da gwamnatin tarayya dangane da bukatun ta.
ASUP, a wata sanarwa dauke da sa hannun sakataren yada labaranta na kasa, Abdullahi Yalwa ta bayyana cewa gwamnati ta biya hudu daga cikin bukatun ta.
Ta ce an yanke shawarar komawa bakin aiki ne domin baiwa gwamnatin tarayya karin lokaci domin biyan sauran bukatu biyar.