Majalisar dokokin jihar Zamfara za ta fara zaman shirin tsige mataimakin gwamnan jihar, Mahdi Aliyu Gusau.
Majalisar na tuhumar mataimakin, wanda ‘da ne ga tsohon Ministan tsaro, Janar Aliyu Gusau, da wasu laifuka.
Kakakin majalisar dokokin jihar Zamfara, Nasiru Magarya, ya umarci magatakardan majalisar, Shehu Anka, ya rabawa dukkan ‘yan majalisa takardar fara shirin tsige mataimakin gwamna, Mahdi Gusau.
A cewar jawabin da mai magana da yawun majalisar, Mustafa Kaura, ya bayyana cewa, an yi hakan bisa sashe na 188 na kundin tsarin mulkin Najeriya.
Kakakin, a cewar jawabin, ya bayyana umarnin a zaman majalisan ranar Laraba, domin baiwa sauran ‘yan majalisa daman karanta laifukan da ake tuhuman mataimakin gwamnan da su.