fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Majalisar dokokin Kaduna za ta binciki Nasir El-Rufa’i

Date:

Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, ta fara binciken lamuni da kuma tallafin da gwamnatin da ta shude ta Mallam Nasir El-Rufai ta karba daga kasashen waje da na cikin gida da ake ta cece-kuce a kai.

Majalisar ta kafa wani kwamiti da zai gudanar da binciken a zauren taron na ranar Talata wanda shugaban majalisar, Yusuf Liman Dahiru ya jagoranta.

An ba wa kwamitin alhakin fara binciken gaskiyar ma’amalar kudi da lamuni da tallafi da sauran ayyukan aiwatarwa tun daga 2015 har zuwa 2023.

Kwamitin binciken ya ba da umarnin gayyatar El-Rufai da wasu manyan mutane ciki har da tsohon shugaban majalisar wakilai ta 8 da ta 9.

Sauran wadanda za a gayyata sun hada da tsoffin kwamishinonin kudi da kuma tsoffin kwamishinonin kasafin kudi da tsare-tsare.

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya koka da dimbin bashin da gwamnatin da ta shude ta bari, wanda ya yi ikirarin gazawa gwamnatin sa.

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp