Majalisar dokokin jihar Zamfara ta tsige, mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Mahdi Aliyu Gusau, daga matsayin sa na mataimakin gwamnan jihar.
Lamarin ya fara samun asali ne sakamakon matsala da gwamnatin jihar Zamfara, tun bayan da gwamnan jihar ya koma jam’iyyar APC, shi kuwa ya ki sauya jam’iyya ya tsaya a ta sa jam’iyyar ta PDP.
Mahdi Aliyu Gusau ya rasa kujerarsa ne, bayan da majalisar dokokin jihar ta zauna a yau Laraba.