Kungiyoyin kwadagon da suka hada da kungiyar kwadago ta Najeriya NLC da kuma TUC sun fara yajin aikin sai baba-ta-gani daga ranar 3 ga watan Yunin 2024.
A cewar kungiyar kwadagon, yajin aikin ya zama dole saboda gwamnatin tarayya ta nuna rashin amincewarta da kin kara Naira 60,000 da ta yi a taron koli na uku da ya gudana a Abuja ranar Juma’a.
Shugaban kungiyar ta NLC, Joe Ajaero da shugaban TUC Festus Osifo ne suka bayyana yajin aikin a wani taron manema labarai na hadin gwiwa.
Osifo ya bayyana cewa, “Kamar yadda kuka sani, mun yi taro na karshe da ya gabata a yau, wato ranar Talata. A wannan taron, sun (gwamnati) sun bayar da Naira 60,000. Sun gayyace mu taro a yau (Juma’a), kuma muka tattauna a kai, muna tunanin suna nuna jajircewar da ya dace.
“Abin mamakinmu, babu wata muhimmiyar wakilci daga Gwamnatin Tarayya ko Gwamnonin Jihohi da ya kamata su kasance cikin tattaunawar.
“Don haka a fasahance, mun ji sun yi watsi da mu saboda sun jajirce game da tayin N60,000. Ko kobo ba a kara masa abin da muka ki yarda da shi ba.”