Kotun koli ta amince da soke rajistar jam’iyyun siyasa 22 da hukumar zabe mai zaman kanta, INEC ta yi.
Hukumar INEC ta soke jam’iyyun ne a shekarar 2020, sakamakon rashin tabuka komai a zabukan da suka gabata.
Mai shari’a Ejembi Eko, wanda ya yanke hukunci a kan lamarin a ranar Juma’a, ya yi watsi da hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke wanda ya soke soke rajistar.
Mai shari’a Eko ya bayyana cewa kotun daukaka kara da kan ta (suo motu) ta tabo batun rashin yin adalci ga wadanda aka soke kuma ta cimma matsaya ba tare da jin ta bakin sauran bangarorin da lamarin ya shafa ba.
“Wannan roko da INEC ta yi ya dace kuma an yarda da haka. Hukuncin kotun da ke kasa an yi watsi da shi,” inji ta.