Labarin dake da ke iske mu yanzu-yanzu, kotun dauka kara dake birnin tarayya Abuja, ta yi watsi da shari’ar kotun da ta yi watsi da zaben tsagin Ganduje.
A baya ne dai cewa, babban kotun tarayya ta bayyana zaben shugabannin APC na Kano na tsagin Malam Ibrahim Shekarau a matsayin sahihi.
Sai dai a yau Alhamis, 17 ga watan Febrairu, kotun daukaka kara ta ce, babbar kotun ba ta da hurumin sauraron karar da tsagin Shekarau ya shigar.
Kotun ta ce lamarin na rikicin cikin jam’yya ne ba na zabe ba, saboda haka uwar jam’iyya ce, za ta yi sulhu tsakanin ‘ya’yan ta.