A ranar Talata ne kotun daukaka kara ta umarci tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello da ya gabatar da kansa domin gurfanar da shi a gaban kuliya.
Kotun ta kuma hana Bello daukar wasu matakai na tuhume-tuhumen, sai dai idan an gurfanar da shi a gaban kuliya.
Kotun ta kuma yi watsi da hukuncin da babbar kotun jihar Kogi ta yanke.
Ba a san inda Bello yake ba tun bayan da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati, EFCC, ta yi yunkurin kama shi a wani samame da suka kai gidansa da ke Abuja, ‘yan watannin da suka gabata.
Gwamna Usman Ododo ya yi fatali da yunkurin jami’an EFCC na kama Bello daga gidansa da ke Abuja.
EFCC na tuhumar Bello da laifin karkatar da sama da Naira biliyan 80 a lokacin yana gwamna na tsawon shekaru takwas.