Kotun sauraren kararrakin zabe ta tabbatar da zaben gwamna Biodun Oyebanji na jihar Ekiti da mataimakinsa Mrs Monisade Afuye.
Kotun da ta yanke hukunci ranar Alhamis a Ado -Ekiti ta yi watsi da karar dan takarar gwamna na jam’iyyar Social Democratic Party (SDP), Mista Segun Oni.
A hukuncin da Shugaban Kotun, Mai Shari’a Wilfred Kpochi da mamba a kwamitin, Mai Shari’a Sa’ad Zadawa suka karanta, sun warware duk wasu batutuwan da suka shafi Oni da jam’iyyarsa ta SDP.
Kwamitin ya ce karar da Oni ya shigar na kin mayar da Oyebanji da Afuye, “ya gaza kai ko wutsiya.”