fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Kotu ta kori ‘yan takarar majalisa 14 na NNPP

Date:

Wata babbar kotun tarayya da ke Fatakwal a ranar Alhamis ta kori ‘yan takarar majalisar dokoki 14 na jam’iyyar New Nigeria People’s Party a jihar Ribas saboda rashin bin dokar zabe da jam’iyyar ta yi wajen gudanar da zabukan fitar da gwaninta.

Jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a jihar ta maka ‘yan takarar jam’iyyar NNPP a gaban babbar kotun tarayya tana neman a soke su.

Alkalin kotun, Mai shari’a Turaki Muhammed, a hukuncin da ya yanke, ya ce jam’iyyar PDP ta iya tabbatar wa kotu cewa jam’iyyar NNPP ba ta bin ka’idojin da aka gindaya a sabuwar dokar zabe a lokacin zaben fidda gwani na jam’iyyarsu.

Don haka alkalin ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta da ta daina amincewa da wadanda abin ya shafa a matsayin ‘yan takara.

Hukuncin na zuwa ne kwanaki kadan bayan wata babbar kotun tarayya da ke Fatakwal ta soke dukkan zabukan fidda gwani da jam’iyyar All Progressives Congress ta gudanar a jihar Ribas.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp