Wata babbar kotun tarayya da ke Fatakwal a ranar Alhamis ta kori ‘yan takarar majalisar dokoki 14 na jam’iyyar New Nigeria People’s Party a jihar Ribas saboda rashin bin dokar zabe da jam’iyyar ta yi wajen gudanar da zabukan fitar da gwaninta.
Jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a jihar ta maka ‘yan takarar jam’iyyar NNPP a gaban babbar kotun tarayya tana neman a soke su.
Alkalin kotun, Mai shari’a Turaki Muhammed, a hukuncin da ya yanke, ya ce jam’iyyar PDP ta iya tabbatar wa kotu cewa jam’iyyar NNPP ba ta bin ka’idojin da aka gindaya a sabuwar dokar zabe a lokacin zaben fidda gwani na jam’iyyarsu.
Don haka alkalin ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta da ta daina amincewa da wadanda abin ya shafa a matsayin ‘yan takara.
Hukuncin na zuwa ne kwanaki kadan bayan wata babbar kotun tarayya da ke Fatakwal ta soke dukkan zabukan fidda gwani da jam’iyyar All Progressives Congress ta gudanar a jihar Ribas.