A ranar Talata ne babban kotun tarayya da ke Abuja, ta kori gwamnan jihar Ebonyi, Dave Umahi, da mataimakinsa, Eric Igwe, daga ofis saboda sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.
Jam’iyyar PDP ta garzaya kotu ta na neman a kori Mista Umahi saboda ya fice daga PDP.
Jaridar Peoples Gazette ta rawaito cewa, kotun ta ce, Mista Umahi da mataimakinsa ba za su iya ci gaba da zama a ofisoshinsu ba, bayan sun koma APC tun lokacin da PDP ta lashe zaben gwamnan jihar Ebonyi a 2019, ba Umahi da Igwe ba.
Mai shari’a Inyang Ekwo ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta da ta daina amincewa da Mista Umahi da mataimakinsa, sannan kuma jam’iyyar PDP ta tura sunayen wadanda za su maye gurbin gwamna da mataimakinsa zuwa INEC.