Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja a ranar Litinin, ta kori dan majalisar wakilai mai ci, Hon Sani Umar Dan Galadima a matsayin dan takarar jamâiyyar PDP mai wakiltar mazabar Kaura Namoda/Birnin Magaji na jihar Zamfara a zaben 2023 mai zuwa.
An fitar da dan majalisar ne daga takarar majalisar wakilai ta 2023 saboda kasancewarsa dan jamâiyyar All Progressives Congress (APC) a lokacin da ya tsaya takarar fidda gwani a PDP.
Mai shariâa Inyang Edem Ekwo ya soke nasarar da dan majalisar ya samu a zaben fidda gwani na jamâiyyar PDP yayin da yake yanke hukunci a karar da wasu jiga-jigan jamâiyyar PDP biyu, Muzammil Mohammed Idris da Ibrahim Sani suka shigar a kansa.
Mai shariâa Ekwo ya bayyana cewa dan majalisar, tun da bai yi murabus ba, ko ya sauya sheka ko kuma ya tsallake rijiya da baya daga APC zuwa PDP a cikin lokacin da doka ta kayyade, ba halalcin dan PDP ba ne, kuma ba zai iya tsayawa takara a kowane zabe a dandalinta ba.
Mai shariâa Ekwo ya yi amfani da sashe na 221 na kundin tsarin mulkin 1999, sashe na 84 na dokar zabe ta 2022 da sashe na 50 (4) na jamâiyyar PDP da su soke zaben fidda gwani na jamâiyyar PDP da ya samar da shi.
Wadanda ake tuhumar sun hada da Hon Sani Umar Dan Galadima, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa INEC, Jamâiyyar PDP da Dr Iyorchia Ayu.
Mai shariâa Ekwo ya bayyana cewa tun daga kan doka ya kamata dan majalisar ya fice daga jamâiyyarsa ta APC kwanaki 30 gabanin zaben fidda gwani na jamâiyyar PDP kafin ya samu damar zama dan takarar PDP.
Kasancewar ya ci gaba da zama a APC a lokacin da ya sayi fom din nuna shaâawa da kuma fom din tsayawa takara a PDP, ya yi kuma ya mika fom din, babu yadda za a yi ya zama dan takarar jamâiyyar.
Daga nan ne alkalin ya bayar da umarnin haramtawa tare da hana dan majalisar bayyana kansa a matsayin dan takarar PDP.
Mai shariâa Ekwo ya sake bayar da wani umarni ga jamâiyyar PDP da ta sake gudanar da sabon zaben fidda gwani da nufin zaben sabon dan takarar mazabar tarayya ta Kaura Namoda/Birnin Magaji a zaben 2023.