fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Kotu ta kori dan majalisar wakilai mai ci kuma dan takara

Date:

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja a ranar Litinin, ta kori dan majalisar wakilai mai ci, Hon Sani Umar Dan Galadima a matsayin dan takarar jam’iyyar PDP mai wakiltar mazabar Kaura Namoda/Birnin Magaji na jihar Zamfara a zaben 2023 mai zuwa.

An fitar da dan majalisar ne daga takarar majalisar wakilai ta 2023 saboda kasancewarsa dan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a lokacin da ya tsaya takarar fidda gwani a PDP.

Mai shari’a Inyang Edem Ekwo ya soke nasarar da dan majalisar ya samu a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP yayin da yake yanke hukunci a karar da wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP biyu, Muzammil Mohammed Idris da Ibrahim Sani suka shigar a kansa.

Mai shari’a Ekwo ya bayyana cewa dan majalisar, tun da bai yi murabus ba, ko ya sauya sheka ko kuma ya tsallake rijiya da baya daga APC zuwa PDP a cikin lokacin da doka ta kayyade, ba halalcin dan PDP ba ne, kuma ba zai iya tsayawa takara a kowane zabe a dandalinta ba.

Mai shari’a Ekwo ya yi amfani da sashe na 221 na kundin tsarin mulkin 1999, sashe na 84 na dokar zabe ta 2022 da sashe na 50 (4) na jam’iyyar PDP da su soke zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP da ya samar da shi.

Wadanda ake tuhumar sun hada da Hon Sani Umar Dan Galadima, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa INEC, Jam’iyyar PDP da Dr Iyorchia Ayu.

Mai shari’a Ekwo ya bayyana cewa tun daga kan doka ya kamata dan majalisar ya fice daga jam’iyyarsa ta APC kwanaki 30 gabanin zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP kafin ya samu damar zama dan takarar PDP.

Kasancewar ya ci gaba da zama a APC a lokacin da ya sayi fom din nuna sha’awa da kuma fom din tsayawa takara a PDP, ya yi kuma ya mika fom din, babu yadda za a yi ya zama dan takarar jam’iyyar.

Daga nan ne alkalin ya bayar da umarnin haramtawa tare da hana dan majalisar bayyana kansa a matsayin dan takarar PDP.

Mai shari’a Ekwo ya sake bayar da wani umarni ga jam’iyyar PDP da ta sake gudanar da sabon zaben fidda gwani da nufin zaben sabon dan takarar mazabar tarayya ta Kaura Namoda/Birnin Magaji a zaben 2023.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaĈ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta Ĉ™addamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Ĉ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaĈ™i...

Najeriya za ta kwashe Ĉ´an Ĉ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, Ĉ™asar...

Iran ta Ĉ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta Ĉ™addamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Ĉ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Ĉ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a Ĉ™asarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Ĉ´an Ĉ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Ĉ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ĉ³an Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin Ĉ´anbindiga da suka addabi yankunan Ĉ™aramar...
X whatsapp