fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Kotu ta bayar da belin Emefiele

Date:

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Legas a ranar Talata ta bayar da belin tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, CBN, Godwin Emefiele.

Kotu ta bayar da belin Emefiele a kan kudi Naira miliyan 20 da kuma wanda zai tsaya masa a daidai wannan adadi.

Hakan ya biyo bayan tuhume-tuhume biyu na mallakar makami ba bisa ka’ida ba da hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta yi masa.

Lauyan Emefiele, Joseph Daudu, bayan da wanda yake karewa ya ki amsa laifuffukan da ake tuhumarsa da su biyu, ya nemi a bayar da belinsa, yana mai cewa laifin da aka tuhumi Emefiele na da beli.

Hukumar DSS dai ta dauko Emefiele ne kimanin wata daya da ya gabata bayan da shugaba Bola Tinubu ya dakatar da shi.

An gabatar da shi kotu ne a wata farar motar kirar Toyota Hilux, dauke da lambar a rufe, da misalin karfe 9:23 na safe.

Da isowar kotun, Emefiele ya sauka daga motar inda wata mata ta taimaka masa a gaban mai shari’a Nicolas Oweibo.

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp