A yanzu haka wasu jiga-jigan ‘yan takarar neman kujerar shugaban jam’iyyar APC na kasa, su na tafka muhawara a Abuja.
Taron da ‘yan jam’iyar ta APC ta shirya ya samu halartar, Sanata Tanko Almakura da Malam Salihu Mustapha da Sanata Ali Modu Sheriff da Sanata Sani Bello, da Sunny Monidafe da Muhammed Etsu da kuma Isa Yuguda da dai sauransu.
‘Yan takarar dai sun gabatar da dalilai daban-daban wadanda dukkansu su ke da nufin zage damtse wajen ganin sun samu matsayi mafi girma a jam’iyya mai mulki.
Jam’iyyar APC ta ce ta shirya taron shekara-shekara mai taken: “APC bayan 2023-ayyukan da ke gabansu: Matsayin masu ruwa da tsaki an yi amfani da shi ne a matsayin mahanga ta basira ga masu neman kujerar shugaban jam’iyyar.
Ku ci gaba da bibiyar mu.