Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta kama wasu da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi da jami’in hukumar NDLEA na bogi.
Wata sanarwa da DSP Suleiman Nguroje ya fitar, ta ce, mutanen da aka bayyana sunayensu kamar haka, Kalbiru Muhammed mai shekaru 41 da kuma Musa Abubakar mai shekaru 29, an kama su ne a lokacin da suke kan hanyarsu ta kai miyagun kwayoyi da aka gano akansu a garin Yola.
An boye magungunan ne a cikin katon talbijin na ledar da akwatin sauti (speaker) don doke jami’an tsaro da kuma gujewa kama su.
Nguroje ya kara da cewa, za a binciki mutumin da aka kama dillalin miyagun kwayoyi da kuma wadanda suka hada da shi da kyau tare da gurfanar da shi a gaban kuliya.